💬
Home Politics Sports Karamar hukumar Garun Malam zata sauyawa kasuwar kwanar Gafan matsuguni

Karamar hukumar Garun Malam zata sauyawa kasuwar kwanar Gafan matsuguni

Sponsored Advert
🔴 Breaking News:

Majalisar karamar hukumar Garun Mallam a jihar Kano ta bai wa mazauna kasuwar Kwanar Gafan wa’adin kwanaki bakwai su tattara kayansu su bar kasuwar nan da ranar 1 ga watan Janairu, 2025.

Sponsored Ad
Sponsored Ad

Wannan umarni ya fito ne daga shugaban karamar hukumar, Barrister Aminu Salisu Kadawa, a yayin kaddamar da shirin sake farfado da tattalin arzikin yankin.

Barrister Kadawa ya bayyana cewa kasuwar ta kauce daga ainihin manufar da ta sa aka kafa ta, inda yanzu aka mayar da ita mafaka da cibiyar ayyukan rashin da’a, maimakon kasuwanci kamar yadda aka tsara tun farko.

Ya gargadi mazauna kasuwar da su bar wurin kafin wa’adin ya cika, tare da jan kunnen cewa duk wanda aka kama ya karya doka, za a dauki matakin hukunci a kansa.

Sponsored

“Nan gaba kadan za mu sanar da ranar da za a sake bude kasuwar bayan an kammala gyare-gyaren da za su mayar da ita ta zamani.

Advertisement

Sponsored
Sponsored Ad - Ad Inserter Pro
Top Advert Bottom Advert

Sabuwar kasuwar za ta bai wa ‘yan kasuwa damar gudanar da harkokin kasuwanci na zamani, wanda zai hada da kayan gona da sauran nau’ikan kayayyakin more rayuwa domin bunkasa tattalin arzikin yankin,” in ji Barr. Aminu Salisu.

Shugaban karamar hukumar ya kuma yi kira ga masu zuba jari su zo su saka hannun jari a sabuwar kasuwar, domin an tsara gyare-gyaren yadda kasuwar za ta dace da bukatun zamani da ci gaba.

© Copyright © 2025 Newspot Nigeria. All rights reserved.
LAGOS WEATHER