💬
Home Politics Sports Tinubu, ka zama mai rikon amana – Limamin Legas

Tinubu, ka zama mai rikon amana – Limamin Legas

Sponsored Advert
🔴 Breaking News:

Babban Limamin Masallacin Juma’a na Lekki, Lagos, Ridhwan Jamiu, ya yi kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya kasance mai rikon amana da adalci ga al’umma a koda yaushe.

Sponsored Ad
Sponsored Ad

Shugaba Tinubu ya halarci sallar Juma’a a Masallacin Juma’a na Lekki tare da sauran masu ibada ranar Juma’a.

Wannan sallar Juma’a ita ce fitowar Shugaban kasa ta farko a bainar jama’a bayan ya dakatar tarukan da aka sbirya yi saboda hadurrukan da suka faru a wasu sassan ƙasar.

Limamin ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su kasance masu gode wa Allah a lokacin ni’ima da kuma haƙuri a lokacin jarabawa.

Sponsored

Limamin ya yi addu’o’i don samun nasarar Shugaban kasa wajen jagorantar Najeriya zuwa ga zaman lafiya, tsaro, da kuma ci gaba.

Advertisement

Sponsored
Sponsored Ad - Ad Inserter Pro
Top Advert Bottom Advert

© Copyright © 2025 Newspot Nigeria. All rights reserved.
LAGOS WEATHER